Anthony Anenih

Ɗan siyasar Najeriya

Anthony Akhakon "Tony" Anenih (4 Agusta 1933 - 28 Oktoba 2018) ɗan siyasan Najeriya ne wanda aka naɗa Ministan Ayyuka da Gidaje a shekara ta 1999.[1]

Anthony Anenih
Minister of Works and Housing (en) Fassara

1999 - 2003 - Adeseye Ogunlewe
Rayuwa
Haihuwa4 ga Augusta, 1933
ƙasaNajeriya
Mutuwa28 Oktoba 2018
Karatu
HarsunaTuranci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'aɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasaPeoples Democratic Party

Rayuwar farko

An haifi Anenih a Uzenema-Arue a garin Uromi, A shekarar 1933 ya shiga aikin ƴan sandan Najeriya a birnin Benin. Yana aiki a gida, ya sami shaidar kammala karatun sakandare. Ya halarci kwalejin ƴan sanda a Ikeja, kuma an zaɓe shi don ƙarin horo a Kwalejin 'yan sanda na Bramshill, Basingstoke, Ingila a 1966 da Makarantar 'Yan sanda ta Duniya, Washington DC a 1970.[2] Ya yi aiki a matsayin ɗan sanda mai bin doka da oda ga Gwamna Janar na farko a Najeriya, Dr. Nnamdi Azikiwe. Ya yi aiki a matsayin malami a kwalejojin ƴan sanda daban-daban, sannan a shekarar 1975 aka tura shi Kwalejin Gudanarwa (ASCON), Legas. Ya yi ritaya daga aikin ƴan sanda a matsayin kwamishinan ƴan sanda.[3]

Farkon siyasa

Anenih ya kasance shugaban jam'iyyar NPN na jihar tsakanin 1981 zuwa 1983, inda ya taimaka wa Dr. Samuel Ogbemudia ya zama gwamnan farar hula na jihar Bendel. Duk da haka, an kwace kujerar gwamna a lokacin da sojoji suka karbe watan Disamba shekara ta 1983. Ya kasance shugaban jam’iyyar Social Democratic Party na ƙasa daga 1992 zuwa 1993, lokacin da ya taimaka wajen zaɓen Cif MKO Abiola a matsayin shugaban ƙasa. Ya kasance memba na taron tsarin mulki a 1994.[3]

Anenih ya kasance mamba a jam'iyyar Peoples Democratic Movement (PDM), United Nigeria Congress Party (UNCP) da kuma People's Democratic Party (PDP). Anenih an ce shi ne ya kitsa sanarwar Shugaba Obasanjo a ranar 26 ga Afrilu, 2002 a babban taron kasa da kasa Abuja.[4] Ya kasance mataimakin kodinetan ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Olusegun Obasanjo na ƙasa a zabukan shekarun; 1999 da 2003.[3]

Ministan Ayyuka da Gidaje

An naɗa Cif Anenih Ministan Ayyuka da Gidaje a shekarar 1999. Daga nan ya zama shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP.[3]

Rigingimu

A watan Oktoban 2009, kwamitin majalisar dattijai ya fitar da rahoto kan binciken da suka yi na amfani da sama da Naira biliyan 300 a harkar sufuri a lokacin gwamnatin Obasanjo. Kwamitin ya ba da shawarar gurfanar da tsoffin Ministoci goma sha uku da suka haɗa da Anenih, inda ya ce ya bayar da kwangiloli ba tare da tanadin kasafin kuɗi ba.[5] A cikin watan Nuwamba 2009, Majalisar Dattijai ta ki amincewa da rahoton ba tare da bata lokaci ba.[6]

A watan Oktoban shekarar 2009, babban bankin Najeriya ya fitar da jerin sunayen abokan hulda da ke da manyan basussuka ga wasu bankuna biyar da aka tantance kwanan nan. Ta ruwaito cewa, ta hanyar Mettle Energy and Gas Limited, Cif Tony Anenih da Osahon Asemota sun ci bashin Naira miliyan 2,065.[7] Anenih ya ce babu ruwansa da kamfanin Mettle Energy and Gas Limited, kuma ya ce ya rubutawa shugabar hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, Farida Waziri, inda ya buƙaci hukumar ta binciki lamarin.[8]

Rayuwa ta sirri

Ya auri Josephine Anenih, lauya, wacce ita ce shugabar ƙungiyar lauyoyin mata daga 1994 zuwa 2000. An naɗa ta a matsayin ministar harkokin mata a ranar 6 ga Afrilun 2010, lokacin da muƙaddashin shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya bayyana sabuwar majalisarsa.[9]

Mutuwa

Anenih ya mutu ranar 28 ga watan Oktoban 2018, kuma an binne shi a mahaifarsa da ke Uromi, inda aka binne shi ya samu halartar manyan mutane a ƙasar. Har zuwa rasuwarsa, shi ne Iyasele na Esan Land.[10]

Manazarta