Ahmed Lemu

Sheikh Ahmed Lemu (1929 - 2020) Malamin Addinin Musulunci ne, Alƙali kuma marubuci a Nijeriya.[1][2][3]

Ahmed Lemu
Rayuwa
HaihuwaJihar Neja, 21 Disamba 1929
ƙasaNajeriya
Mutuwa24 Disamba 2020
Ƴan uwa
Abokiyar zamaAisha Lemu
Karatu
MakarantaUniversity of London (en) Fassara
HarsunaTuranci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'ailmantarwa
Kyaututtuka

Rayuwar farko da ilimi

An haifi Shaikh Ahmed Lemu a garin Lemu Jihar Neja, Nijeriya, a ranar 21 ga watan Disamba, 1929. Ya fara karatun firamare a makarantar Alkur'ani a shekarar 1932, sannan ya halarci makarantar firamare a shekarar 1939. Daga nan ya shiga makarantar sakandare (Kwalejin Gwamnati) a Lemu, inda ya sami difloma a makarantar sakandare a shekara ta 1948. Daga baya ya shiga makarantar koyan aikin lauya da ke Lemu inda ya sami takardar shedar koyarwa ta tsakiya a shekarar 1950 da kuma digiri na biyu a shekarar 1952.

A shekara ta 1954, ya tafi Ingila karatu a Jami'ar London ta Makarantar Afirka da Gabas ta Tsakiya inda ya sami Babban Ilimin (Advanced Level) a Tarihi, Larabci, Hausa da Yaruka a 1961, ya sami Digiri na biyu a Afirka da kuma Nazarin Gabas a shekarar 1964.[4][5][6]

Ayyuka

Lemu ya koyar da Larabci, Turanci da karatun addinin Musulunci a makarantar sakandaren gwamnati da ke Bida tsakanin 1953 da 1960. Ya zama Shugaban Kwalejin Malamai ta Arabiyya a 1970, da kuma Babban Sufurtanda na Ilimi a Arewa maso Gabas, Yammacin Nijeriya tsakanin 1971 da 1973. Ya kuma yi aiki a matsayin Daraktan Fasaha (1974-1975) da Daraktan Tsare Tsare na Ilmi (1975-1976) a Jihar. A shekarar 2009, an nada shi mai ba da shawara a Jami’ar Fountain da ke Osogbo, Najeriya. Baya ga rawar da ya taka a bangaren koyarwa da koyo, Lemu ya kuma yi aikin lauya, a matsayin Alkali a Kotun daukaka kara a Jihohin Sakkwato da Neja (1976-1977) da kuma Babban Alkalin Kotun ɗaukaka kara a Jihar Neja. (1976-1991).[7][8][9]

Manazarta