Fatima

Yar Annabi matan Ali

Fāṭima bint Muḥammad ( Larabci: فَاطِمَة ٱبْنَت مُحَمَّد‎ , 605/15–632 CE), wanda aka fi sani da Fāṭima al-Zahrāʾ ( فَاطِمَة ٱلزَّهْرَاء ), ta kasance diyar annabin musulunci Muhammad da matarsa Khadija . [1] Mijin Fatima shi ne Ali, shine na hudu a cikin Khalifofin Rashidun kuma Imamin Shi'a na farko . 'Ya'yan Fatima su ne Hasan da Husaini Imaman Shi'a na biyu da na uku. [2] [3]

Fatima
Rayuwa
HaihuwaMakkah, 27 ga Yuli, 604
ƙasaKhulafa'hur-Rashidun
Harshen uwaLarabci
MutuwaMadinah, 14 Disamba 632
MakwanciAl-Baqi'
Ƴan uwa
MahaifiMuhammad
MahaifiyaKhadija Yar Khuwailid
Abokiyar zamaSayyadina Aliyu
Yara
AhaliUmmu Kulthum, Rukayyah, Zainab yar Muhammad, Ibrahim ɗan Muhammad, Yaran Annabi da Abdullahi ɗan Muhammad
Karatu
HarsunaLarabci
Sana'a
Sana'amaiwaƙe
Imani
AddiniMusulunci

An kwatanta Fatima da Maryamu mahaifiyar Isah, musamman a aqidar Shi'a. [4] [5] An ce Muhammadu ya dauke ta a matsayin mafificiya a mata [2] [6] kuma mafi soyuwa a gare shi. [7] [2] Sau da yawa ana kallonta a matsayin babban abin tarihi ga matan musulmi da kuma ita me tausayi, karimci, da jurewa wahala. [4] Ta hanyar Fatima ne zuriyar Muhammadu suka wanzu har yau. [8] [6] Sunanta da lakabinta sun kasance sanannen zaɓi ga 'yan mata musulmai. [9] [10]

Lokacin da Muhammadu ya rasu a shekara ta 632, Fatima da mijinta Ali sun ƙi amincewa da mulkin khalifa na farko, Abubakar . Ma'auratan da magoya bayansu sun yi imanin cewa Ali shi ne mafi cancantar magajin Muhammadu, [4] mai yiwuwa suna nufin sanarwarsa a Ghadir Khumm . [11]

Rigima ta kunno kai dangane da mutuwar Fatima a cikin watanni shida da mutuwar Muhammadu. [8] Ahlus Sunna sun yarda cewa Fatima ta rasu ne da bakin ciki. [3] A cikin Shi’a kuwa, an ce mutuwar Fatima (barin da tayi) ta yi ne kai tsaye sakamakon raunukan da ta samu a lokacin wani farmaki da aka kai gidanta don murkushe Ali, wanda Abubakar ya umarta. [2] An yi imanin cewa fatawar Fatima da ta rasu shi ne kar khalifa ya halarci jana’izarta. [12] [13] An binne ta a asirce da daddare kuma ba a tabbatar da ainihin inda aka binne ta ba. [14] [15]

Suna da laƙabi

Mafi sanannan laƙabinta shi ne al-Zahra ( lit. 'me haskakawa', 'me haske ' ), [2] wanda ke nuni akan taqawarta da tsayuwarta a cikin addu'a. [16] Shi'a sun yi imani da wannan taswirar cewa tana nuni ne ga halittarta ta farko daga hasken da ke ci gaba da haskakawa a cikin halittu. [2] Shi'a Ibn Babawahy ( d. 991 ) ya rubuta cewa, duk lokacin da Fatima ta yi addu'a, haskenta yana haskakawa ga mazauna sama kamar yadda hasken taurari ke haskaka mazaunan duniya. [7] Sauran lakabin ta a cikin Shi'a su ne al-Shiddiqa ( lit. 'me gaskiyta ' ), [10] al-Tahira ( lit. 'me tsarki' ), [1] al-Mubaraka ( lit. 'me albarka' ), [1] da al-Mansura ( lit. 'wanda Allah ya taimaka' ). [2] Wani lakabin Shi'a kuma shi ne al-Muḥadditha, bisa la'akari da rahoton cewa mala'iku sun yi magana da Fatima a lokuta da dama, [17] [18] [19] kamar Maryamu mahaifiyar Isah . [18]

Manazarta

🔥 Top keywords: