Borno

jiha a Najeriya
(an turo daga Jihar Borno)

Jihar BornoAbout this soundBorno  jiha, ce dake arewa maso gabashin Najeriya. Ta haɗa iyaka da Jihar Yobe daga yamma, Gombe daga kudu maso gabas, Adamawa daga kudu, yayin da iyakarta ta gabas ta.hada iyaka ta kasa da kasa da Kamaru, iyakarta ta,arewa kuwa ta hade ne da yankin kasar Nijar, sannan iyakarta ta arewa maso gabas ta hade ne da yankin ƙasar Chadi, ita kadai ce jihar da ta haɗa iyaka da kasashen waje har guda uku. Jihar ta samo asalin sunanta ne daga Masarautar Borno mai dumbin tarihi, tare da tsohuwar babban birnin masarutar dake Maiduguri. An ƙirƙiri jihar ne a shekarar alif 1976, lokacin da aka raba tsohuwar Jihar Arewa ta Gabas. A farko jihar ta haɗa da yankin Jihar Yobe ta yau, wacce aka raba ta a Shekarar alif 1991.[1]

Borno
Borno State (en)


Wuri
Map
 11°30′N 13°00′E / 11.5°N 13°E / 11.5; 13
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya

Babban birniMaiduguri
Yawan mutane
Faɗi5,860,183 (2016)
• Yawan mutane82.66 mazaunan/km²
Harshen gwamnatiTuranci
Labarin ƙasa
Yawan fili70,898 km²
Sun raba iyaka da
Bayanan tarihi
MabiyiJihar Arewa maso Gabas
Ƙirƙira3 ga Faburairu, 1976
Tsarin Siyasa
Majalisar zartarwaexecutive council of Borno State (en) Fassara
Gangar majalisaMajalisar Wakilan jihar Borno
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci
Lamba ta ISO 3166-2NG-BO
Wasu abun

Yanar gizobornostate.gov.ng
jiha mai dumbin mutane da kuma al'adu
People of Borno
Umar Borno
cikin garin Borno

Jihar Borno ita ce jiha ta biyu 2 a.girman ƙasa a cikin jihohi 36 na Najeriya, bayan Jihar Neja. Amma duk da girman jihar, ita ce ta goma Sha daya (11) a yawan mutane tare da kiyasin mutane a kalla miliyan 5.86 a shekara ta alif 2016.[2] A fannin yanayin kasa; semi-desert Sahelian savanna daga arewa da kuma Sudanian savanna ta yamma a tsakiya da kudancin jihar, da kuma mutane Mandara Plateau daga yankin kudu maso gabas.

Jihar Borno tana da kabilu da suke zaune a yankin na lokaci mai tsawo, kamar su Dghwede, Glavda, Guduf, Laamang, Mafa, da Mandara a tsakiyar yankin; Afade, Yedina (Buduma), da kuma Kanembu daga karshen yankin arewa maso gabas; harshen Waja a kuryar kudancin yankin; da kuma Kyibaku, Kamwe, Kilba, Margi da kuma babur a yankin kudancin jhar, a yayinda harsunan Kanuri da Shuwa Arab ke rayuwa a yankunan tsakiya da arewacin jihar. Ta fannin addini, mafi yawan mutanen jihar (85%) musulmai ne, da tsirarun kiristoci da mabiya addinan gargajiya da kaso 7% kowanne.

Tun daga karni na bakwai (07), inda aka sani da Jihar Borno ta kasance daga yankin Daular Kanem-Bornu. Daular da ta fito daga yankin kudancin Libya ta yau (Fezzan) har zuwa yankin Cadi har zuwa yankin Jihar Borno ta yau. Bayan karni na 13, an tilasta wa Kanem Bornu matsawa bayan yaƙoƙi da ba suyi nasara ba, inda ta koma Masarautar Borno, kafin ta kara karfi kuma ta mulki yankin har na tsawon shekaru 500. Har sai zuwa karni na 18 (shekara ta 1800) lokacin Jihadin Fulani suka raunata Masarautar Bornu, har masarautar ta fara rage karfi. An kwace mafi yawancin yankin masarautar inda aka hade ta da yankin Jihar Adamawa ta yau a karkashin Daular Halifancin Sokoto. Shekaru 80 bayan haka, Rabih az-Zubayr, wani kusan yaki dan kasar Sudan ya mallake Daulana Shekarar kuma ya mulke ta har zuwa karni na Shekarar alif 1900 lokacin da sojojin Faransa suka kashe shi a Yakin Kousséri. Har wayau, turawan mulkin mallaka sunci Masarautar Adamawa da yaki, inda Daular Jamus da na Burtaniya suka ci su da yaƙi. Duka yankunan kasar Rabih da kuma Masarautar Adamawa an rabasu tsakanin turawan mulkin mallaka inda sashin Masarautar Borno ta yau ta fada karkashin mulkin Jamus da Burtaniya.

An hade yankin da Burtaniya ke da iko ta Yankin Mulkin Mallaka na Arewacin Najeriya wacce daga baya aka hade ta ta zamo Yankin Mulkin Mallaka ta Najeriya, wacce daga baya ta samu 'yanci a Shekarar alif 1960, Najeriya. Yankin da kasar Jamus ke da iko kuwa (yankin dake kusa da iyakar Kamaru ta yau) ta zamo Bornu-na mutanen Jamus a matsayin yankin "German-Kemerun har zuwa lokacin da sojojin hadin gwiwa suka kai farmaki a yankin a lokacin kamfe na Kamerun a lokacin Yakin duniya ta daya. Inda ke matsayin farfajiyar Jihar Borno daga gabas a yau ta zamo sashin Arewacin Kamaru a karkashin yankin Kamaru ta Burtaniya har zuwa shekarar 1961, a lokacin da wata yarjejeniya ta jawo aka hadeta cikin yankin Najeriya. Daga farko, bayan samun 'yanci, sashin Jihar Borno na daga cikin yankin Jihar Arewa ta Gabas. Bayan an raba Jihar Arewa ta Gabas, an kirkiri Jihar Borno a ranar 3 ga watan Febrerun na Shekarar alif 1976 tare da sauran jihohi guda goma. Shekaru goma sha biyar bayan yi mata jiha, an hade wasu kananan hukumomi daga yammacin jihar don samar da Jihar Yobe. Bayan wasu 'yan shekaru, a cikin shekara ta 2000, Jihar ta zamo cibiyar kungiyar Boko Haram kuma daga nan ta fara samar da rudani a shekara 2009. A tsakanin shakara ta 2012 zuwa 2015, abin yayi kamari a yankin yayinda kusan akasarin ikon jihar ta koma karkashin kungiyar, hakan yasa kungiyar ta zama mafi munin kungiya a duniya kuma sun sa mutum sama da miliyan sun bar gidajensu da dukiyoyinsu. Bayan munanan hare-hare a cikin jihar a shekara ta 2015 da kuma fada tsakanin kungiyar Boko Haram da na ISWAP, an kore kungiyoyin zuwa cikin Dajin Sambisa da wasu tsiburai da ke yankin Tabkin Chadi a shekara ta 2017; har wayau, rashin zaman lafiya a yankin ya zama ruwan dare yayinda 'yan ta'adda ke kai hare-hare ga sojoji da farar hula baki daya.[3]

A matsayinta na jiha da ta dogara ta wata fuskar da noma da kiwo, tattalin arzikin yankunan karkarar Jihar Borno sun dogara ne akan noma da kiwo kafin soma rikicin Boko Haram, yayinda babban birnin jihar wato Maiduguri take taka muhimmiyar rawa a matsayin cibiyar kasuwanci da kuma hada-hada.[4] Amma duk da haka, bayan shekaru da jihar ta sha fama da rashin zaman lafiya, wanda ya kawo cikas ga cigaba kuma ya tilasta wa manoma suka bar kauyukansu don neman tsira, Jihar Borno tana na goma sha uku a jerin cigaban al'umma a kasar, amma tunda an fara shawo kan rikicin a shekara ta 2016, an fara farfado da harkokin cigaba a yankin.[5][6][7]

Jihar Borno da faɗin ƙasa kimanin kilomita 57,799 da yawan jama’an da suka kai kimanin mutane 5,925,668 (a ƙiddidigar ƙidaya ta shekara ta 2006).Babban birnin jihar shi ne Maiduguri. Babagana Umara Zulum shi ne gwamnan jihar tun bayan zabensa da aka yi a shekara ta 2019 har zuwa yau. Mataimakin gwamnan kuwa shi ne Usman Mamman Durkwa. Dattijai daga jihar sun haɗa da: Yusuf Buratai, Baba Garba, Ali Madu Sheriff, Muhammad Indimi, Abba Kyari, Mohammed Ali Ndume da sauransu. Mutanen garin Borno mutane ne masu son al'ada da kokarin riko da addini da fafutuka wajen neman ilimi. Daga cikin al'adunsu akwai zaman mai gida wuri daya tare da iyalensa domin cin abinci a cikin faranti/kwano daya. Mutane ne masu son mu'amala da turare sannan matan su suna yawan yin kwalliya, lalli wato dayes da dai sauransu. Akan samu yaruka mazauna Borno kamar irin su Kanuri, Babur, margi, da dai sauransu.

Tarihi

Mutanen Kanuri sune ƙabilar da ta fi ƙarfi a Jihar Borno, bayansu akwai ƙabilu kamar Lapang, Babur/Bura da Marghi wanda ake samu a yankin kudancin jihar. Kabilar Shuwa Arab mafi akasarinsu sun samo asaline daga Larabawa.[8] Sarakunan tsohuwar yankin Daular Kanem-Bornu sun taka muhimmiyar rawa a siyasan wannan yankin na kusan shekaru 1000.[9]

Masarautar Kanemi ta yanzu amshe ikon Masarautar Borno a farkon karni na 19 bayan yakin Jihadin Fulani na Shehu Usman Dan Fodiyo. Rabih az-Zubayr ya mulke ta a Shekarar 1893.[10] Burtaniya, Faransa da Jamus sun kai farmaki a yankin a farkon karni na 20. Acikin shekarar 1902 ne, Burtaniya ta sanya jihar cikin Yankin Mulkin Mallaka na Arewacin Najeriya,[11] sannan a Shekarar 1907, suka kafa babban birnin a Maiduguri, wacce ta tsaya matsayin babban birinin jihar har yau.[12]

Bayan samun 'yancin Najeriya a Shekarar 1960, Jihar Borno ta kasance kasa mai 'yancin kai har zuwa lokacin da aka kafa jihohi 12 a Shekarar 1967. Sabon tsarin kananan hukumomi na shekarar 1976, ya rage wa sarakuna karfin iko a masarautar sannan a lokacin da Najeriya ta dawo mulkin farar hula a Shekarar 1979, karfin mulki sarakuna sun koma a fannin al'adu da gargajiya ne kawai. An zabi Mala Kachalla a matsayin gwamnan jihar a shekarar 1999, a karkashin jam'iyyar APP (All Peoples Party), wacce daga baya ta koma ANPP (All Nigeria People's Party). Sannan a watan Aprelun 2003 ne aka zabi Ali Modu Sheriff a matsayin gwamnan Jihar Borno.[13]

Rikicin Boko Haram ya soma ne a shekara ta 2009, tare da Jihar Borno a matsayin yankin da abu yafi shafa. A ranar 14 ga Watan Mayun shekara ta 2013 ne, Shugaba Goodluck Jonathan ya sanar cewa an sanya takunkumi a yankunan arewa maso gabashin Najeriya, wanda ya hada da Jihar Borno da makwabtanta jihohin Adamawa da Yobe.[14] Wannan ya faru ne bayan rikici tsakanin 'yan Boko Haram da sojojin Najeriya ya jawo mutuwar rayukan mutum 200 a yankin birnin Baga. Wani mai magana daga sojojin Najeriya ya sanar cewa zasu cigaba da kai farmaki har sai sunga bayan ta'addanci a kowanne a sashe a Najeriiya.[15]

Acikin watan Yuli shekarar 2014 ne, gwamna Kashim Shettima ya sanar cewa, "an kashe malamai 176 kuma an lalata makarantu fiye da 900 tun fara rikicin a shekara ta 2011. An kulle mafi yawancin makarantun Jihar Borno bayan garkuwa da akayi da dalibai mata daga Chibok a watan Afrilu shekarar 2014.

Acikin watan Nuwamban shekarar 2014 ne, UNICEF ta sanar da cewa ta kara yawan cibiyoyinta na tallafawa akan karancin kumari (Community Management of Acute Malnutrition) na daga rashin cin abinci mai gina jiki a Jihar Borno daga "5 zuwa 67".[16] Sashin noma na jihar ta samu babban cikas musamman a dalilin rashin zaman lafiya kuma mutane da dama sun shiga hali na rashin tsaro ta fuskar abinci.[17]

ruwan baga dake jihar borno

Ƙananan Hukumomin Borno

Jihar Borno:jiha ce da take da kananan hukumomi guda ashirin da bakwai (27) Su ne kamar haka:[18]

Borno Central
Senatorial District
Area in
km2
1,666,541Borno South
Senatorial District
Area in
km2
1,245,962Borno North
Senatorial District
Area in
km2
1,238,390
Maiduguri137.36540,016Askira/Uba2,431.83143,313Abadam4,172.27100,065
Ngala1,519.82236,498Bayo985.7879,078Gubio2,575.09151,286
Kala/Balge1,962.1360,834Biu3,423.86175,760Guzamala2,631.4495,991
Mafa2,976.99103,600Chibok1,392.0066,333Kaga2,802.4689,996
Konduga6,065.89157,322Damboa6,426.18233,200Kukawa5,124.41203,343
Bama5,158.87270,119Gwoza2,973.15276,568Magumeri5,057.61140,257
Jere900.72209,107Hawul2,160.99120,733Marte3,280.02129,409
Dikwa1,836.89105,042Kwaya Kusar754.6956,704Mobbar3,280.02116,633
Shani1,238.93100,989Monguno1,993.20109,834
Nganzai2,572.3599,074

Bugu da kari akwai gundumomin masarautu guda takwa a jihar (Borno, Damboa, Dikwa, Biu, Askira, Gwoza, Shani da kuma masarautar Uba).[19] Wanda suke baiwa kananan hukumomi shawarwari na al'adu da gargajiya.[20]

Harsuna

Harsunan da ake amfani dasu a Jihar dangane da kananan hukumominsu sun hada da:[21]

LGALanguages
Askira-UbaPutai; Bura-Pabir; Gude; Kibaku; Marghi Central; Marghi South; Nggwahyi; Nya Huba; Marghi
BamaShuwa Arabic; Yerwa Kanuri; Wandala; Mafa; Marghi
BiuBura-Pabir; Dera; Ga'anda; Jara; Putai, Marghi
ChibokKibaku; Putai; Marghi
DamboaKibaku; Marghi Central; Putai; Mulgwai; Kanuri
DikwaShuwa Arab
GwozaCineni; Dghwede; Glavda; Guduf-Gava; Gvoko; Hide; Yerwa Kanuri; Lamang; Mafa; Sukur; Waja; Wandala; Marghi
HawulBura,Hwana, Putai mafa; Marghi
Jilbe townJilbe
KagaYerwa Kanuri; Putai
Kala/BalgeShuwa Arab; kanuri; Afade
KondugaShuwa Arab; Yerwa Kanuri; Maffa; Putai; Wanda; Marghi
KukawaYerwa Kanuri
Kwaya-KusarBura, Putai, Marghi South
MaiduguriYerwa Kanuri; Mafa
MongunoYerwa Kanuri; Mafa
NgalaShuwa Arab; Yerwa Kanuri

Sauran yarukun Jihar sune: Lala-Roba, Tarjumo, Yedina, da kuma Tedaga.[22]

Addinai

Mafi yawancin mutanen Jihar Borno musulmai ne, tare da tsirarun mabiya addinin kirista da waninsu. Ana amfani da shari'ar musulunci a harkokin ci gaba, zamantakewa, addini da dai sauransu.

Masana'antu

Masana'antu a jihar Borno nada yawa , wasu daga ciki sun gada da:

  • Masana'antar Borno textile
  • Masana'antar Flex Foam Nigeria Ltd
  • Masana'antar Simba Industry Ltd[23]

Ilimi

Jihar Borno nada cibiyoyin ilimi ma bam-banta, wadannan sun hada da:

Jami'o'i

  • Univeristy of Maiduguri[24]
  • Nigerian Army University Biu[25]
  • Borno State University[26]
  • Al-ansar University[27]
  • Kashim Ibrahim College of Education
  • Mohammed Goni College of Legal and Islamic Studies[28]
  • Maiduguri Colege of Nursing and Midwifery[29]

Ma'adinai

Jihar Borno nada tarin albarkatun ƙasa da ma'adinai masu tarin yawa , sawu daga cikinsu sun haɗa da:[30]

  • Laka
  • Ma'adanin Kaolin
  • Ma'adanin Diatonite
  • Ma'adanin Trona
  • Ma'adanin Iron
  • Ma'adanin Mica
  • Ma'adanin Quartz
  • Ma'adanin Magnetite
  • Ma'adanin Uranium

Shahararrun Mutane

Ibrahim Ibn Al-hussaini

  • Zakariya Maimalari, Sojan Najeriya
  • Mohammed Indimi, Dan kasuwa
  • Kyari Magumeri, soja
  • Fiona Lovatt, mai bibiyar 'yancin mutum
  • Shaykh Sherif Ibrahim Ibn Saleh al-Hussaini, Malamin addinin musulunci kuma Mufti
  • Abba Kyari dan kasuwa, dan siyasa
  • Abba Kyari (military general), jenar na soja
  • Kashim Shettima, [31]mataimakin shugaban kasa
  • Sheikh Abba Aji Babban malamin addin
  • Professor Babagana Umara Zulum, Gwamnan jahar[32]

Manazarta


Jihohin Najeriya
Babban birnin tarayyar (Abuja) | Abiya | Adamawa | Akwa Ibom | Anambra | Bauchi | Bayelsa | Benue | Borno | Cross River | Delta | Ebonyi | Edo | Ekiti | Enugu | Gombe | Imo | Jigawa

Kaduna | Kano | Katsina | Kebbi | Kogi | Kwara | Lagos | Nasarawa | Neja | Ogun | Ondo | Osun | Oyo | Plateau | Rivers | Sokoto | Taraba | Yobe | Zamfara

🔥 Top keywords: